Kotu ta tsare fitaccen ɗan daudun Tiktok, Abubakar Kilina, a Kano bisa zargin sanya kayan mata da ɗabi’ar batsa

Wata kotun majistare da ke a Kano ta bayar da umarnin tsare wani fitaccen ɗan TikTok, Abubakar Kilina, bisa zargin sanya kayan mata da kuma wallafa abubuwan da suka saba da tarbiyya da addini a shafinsa na sada zumunta.

A cewar hukumar tace fina-finai da ɗabi’u ta Jihar Kano, wacce ta shigar da ƙarar, Kilina ya saba da ƙa’idar ɗabi’a da al’adu na jihar ta hanyar yin shigar mata da furta kalmomin batsa a kafafen sada zumunta, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’umma.

Mai magana da yawun hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, inda ya ce laifin Kilina ya sabawa doka, kuma za su ci gaba da sa ido kan masu amfani da kafafen zamani wajen yaɗa abinda ya saba wa al’adun jihar.

Abubakar Kilina ya amsa laifinsa a gaban kotu, yayin da Lauya Garzali Maigari Bichi ya jagoranci gurfanar da shi. Alƙaliya Hajiya Halima Wali ce ta jagoranci zaman kotun, inda ta bayar da umarnin tsare Kilina daga ranar 4 zuwa 17 ga Yuni, 2025, domin ci gaba da sauraren ƙarar.

A cewar babban sakataren hukumar tace fina-finai ta jihar, Alhaji Abba El-Mustapha, gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yakar duk wani abu da ke ƙoƙarin rugujewar tarbiyya da ɗabi’un jama’a, musamman a kafafen intanet.

Ya ƙara da cewa Abubakar Kilina ba shi ne na farko ba da aka kama bisa irin wannan laifi, domin kuwa akwai wasu da dama da aka gurfanar da su bisa tuhuma iri ɗaya a ‘yan watannin da suka wuce.

More from this stream

Recomended