Kotu ta tabbatar da zaben Dauda Lawal Dare a matsayin gwamnan Zamfara

Kotun sauraren kararrakin zaɓen gwamnan jihar Zamfara ta tabbatar da nasarar da gwamnan jihar Dauda Lawal ya samu a zaɓen da aka gudanar..

Lawal ya yi nasara kan abokin takararsa kuma gwamna mai ci, Bello Matawalle a zaben gwamnan jihar na ranar 18 ga watan Maris.

Matawalle wanda a yanzu shi ne karamin ministan tsaro n ya garzaya gaban kotun inda yake kalubalantar sakamakon zaben.

A hukuncin ta na ranar Litinin kotun ta ayyana cewa karar bata ta da hujja.

Kotun tavkuma bayar da umarnin a biya wanda ake kara kudi har naira 500, 000.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Yan sanda sun gano haramtacciyar masana’antar ƙera makamai Cross River

Rundunar yan sandan jihar Rivers ta ce ta bankaɗo wata haramtacciyar masana'antar ƙera bindigogi da nakiyoyi dake garin Osomba a karamar hukumar Akamkpa ta...