Kotu ta tabbatar da zaben Dauda Lawal Dare a matsayin gwamnan Zamfara

Kotun sauraren kararrakin zaɓen gwamnan jihar Zamfara ta tabbatar da nasarar da gwamnan jihar Dauda Lawal ya samu a zaɓen da aka gudanar..

Lawal ya yi nasara kan abokin takararsa kuma gwamna mai ci, Bello Matawalle a zaben gwamnan jihar na ranar 18 ga watan Maris.

Matawalle wanda a yanzu shi ne karamin ministan tsaro n ya garzaya gaban kotun inda yake kalubalantar sakamakon zaben.

A hukuncin ta na ranar Litinin kotun ta ayyana cewa karar bata ta da hujja.

Kotun tavkuma bayar da umarnin a biya wanda ake kara kudi har naira 500, 000.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]