Kotu ta tabbatar da nasarar da Rufa’i Sani Hanga ya samu

Kotun sauraren kararrakin zaben yan majalisar tarayya da na jihohi dake zamanta a Kano ta tabbatar da nasarar zaben da Sanata Rufa’i Sani Hanga ya samu na jam’iyar NNPP a zaben mazabar Kano ta tsakiya.

Dantakarar jam’iyar APC a zaben ranar 25 ga watan Faburairu, Abdulsalam Abdulkarim wanda aka fi sani da AA zaura shi ne ya shigar da kara gaban kotun inda yake kalubalantar ayyana Sanata Rufa’i Sani Hanga na jam’iyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben kujerar sanatan Kano ta tsakiya.

Zaura ta bakin lauyansa, Ishaka Dikko ya roki kotun da ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben kuma ta jingine sanarwar da INEC ta yi da ya bawa Hanga nasara.

Da yake yanke hukuncin ranar Litinin jagoran rukunin alkalan da suka jagoranci zaman shari’ar, mai shari’a I.P Chima ya ce mai karar ya gaza tabbatar da zargin da yake yi ciki har da rashin bin ka’idar dokokin zabe saboda haka an kori karar.

Har ila yau kotun ta bada umarnin mai kara ya biya naira 300, 000 ga wadanda ake kara wato INEC, Hanga, NNPP da kuma Ibrahim Shekarau

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...