Kotu ta sake soke zaɓen ɗan majalisar tarayya na NNPP a Kano

Kotun sauraren kararrakin zaben yan majalisar tarayya da na jiha a jihar Kano ta tabbatar da cewa ɗan majalisar wakilai ta tarayya dake wakiltar karamar hukumar Kumbotso Mukhtar Dan Kawu ya yi amfani da takardar kammala sakandare ta jabu da yayi amfani da ita wajen tsayawa takara.

Abokin takararsa Munnir Dan Agundi na jam’iyar NNPP ya shigar da kara inda ya roki kotun da ta ayyana cewa Dan Kawu ya yi amfani da takardar kammala sakandare ta jabu wajen shiga makarantar Kaduna Polytechnic.

A hukuncin da kotun tayi alkalan kotun su uku ƙarƙashin jagorancin mai shari’a I. P Chima ta tabbatar da cewa Idris Dankawu ya yi jabun takardar WAEC a saboda haka ta soke zaben sa.

Kotun ta umarci hukumar zabe ta INEC ta jingine shedar cin zaben da ta bawa Dankawu kuma ta ayyana Mannir Babba na jam’iyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...