Kotun sauraren kararrakin zaben yan majalisar tarayya da na jiha a jihar Kano ta tabbatar da cewa ɗan majalisar wakilai ta tarayya dake wakiltar karamar hukumar Kumbotso Mukhtar Dan Kawu ya yi amfani da takardar kammala sakandare ta jabu da yayi amfani da ita wajen tsayawa takara.
Abokin takararsa Munnir Dan Agundi na jam’iyar NNPP ya shigar da kara inda ya roki kotun da ta ayyana cewa Dan Kawu ya yi amfani da takardar kammala sakandare ta jabu wajen shiga makarantar Kaduna Polytechnic.
A hukuncin da kotun tayi alkalan kotun su uku ƙarƙashin jagorancin mai shari’a I. P Chima ta tabbatar da cewa Idris Dankawu ya yi jabun takardar WAEC a saboda haka ta soke zaben sa.
Kotun ta umarci hukumar zabe ta INEC ta jingine shedar cin zaben da ta bawa Dankawu kuma ta ayyana Mannir Babba na jam’iyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.