Kotu ta mayar da Emefiele gidan waƙafi

Mai shari’a Hamza Muazu na babbar kotun tarayya dake babban birnin tarayya Abuja, ya bayar da umarnin tsare tsohon gwamnan babban bankin Najeriya CBN Godwin Emefiele a gidan yari na Kuje har sai an kammala tantance bukatarsa ta neman beli.

Emefiele zai ci gaba da zama a gidan yari har zuwa ranar 22 ga watan Nuwamba, lokacin da kotu za ta yanke hukunci kan bukatar belinsa.

Lauyan sa, Mathew Burkaa SAN, ya gabatar da bukatar neman belin wanda Rotimi Oyedepo ya yi kakkausar suka a madadin gwamnatin tarayya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]