Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam’iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam’iyar.

Mai Shari’a  Peter Lifu shi ne ya bayar da umarnin gaggawar a ranar 3 ga watan Mayu da ya hana jam’iyar zaɓar wani mutum domin ya maye gurbin Damagum har sai an kammala shari’ar da aka shiga gabansa.

Umar El-Gash Maina and Zanna Mustapha Gaddama sune suka shigar da ƙarar mai namba FCH/ABJ/CS/579/2024 a gaban kotun ranar 2 ga watan Mayu.

Waɗanda ake ƙara a shari’ar sun haɗa da kwamitin zartarwar jam’iyar, kwamitin amitattun jam’iyar, shugabannin jam’iyar da kuma hukumar zaɓe ta INEC.

Kotun ta dage sauraron ƙarar ya zuwa ranar 14 ga watan Mayu.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...