Kotu ta hana Ganduje sayar da asibiti

Kotu ta dakatar da gwamnatin Kano daga sayar da asibitin yara da kuma haihuwa dake unguwar Yan Awaki a cikin babban birnin jihar.

Mai sharia Maryam Sabo ta babbar kotun jiha mai lamba 16 dake Miller Road ce ta bayar da umarnin kan karar da al’ummar unguwar suka kai gaban ta.

Salisu Ibrahim Yan Awaki shi ne ya shigar da karar amadadin wasu mazauna unguwar su 113.

Lauyan mutanen yan Awaki Barista Badamasi Sulaiman Gandu ya roki kotun da ta dakatar da gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje da Antoni Janar na jihar da kuma karamar hukumar Birni da Kewaye daga shirin su na sayar da asibitin.

Mai shariar ta amince da bukatar mutanen unguwar inda ta bukaci mutanen da ake kara da su dakata har sai ranar da za ta sake sauraron karar.

More News

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 191 tare da kama 184

Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana hakan ne a wata sanarwa wacce aka fitar bayan wani taron manema labarai da rundunar ta yi a Abuja...

Farashin gangar ɗanyen man fetur ya ƙaru zuwa $97

Farashin É—anyen man fetur ya karu sosai a ranar Alhamis inda aka rika sayar da kowacce ganga kan dalar Amurka $97. Farashin man nau'in Brent...

Kungiyar ƙwadago ta NLC ta dage kan tsunduma yajin aiki

Kungiyar ƙwadago ta NLC ta ce babu wata yarjejeniya da ta shiga da gwamnatin tarayya domin ta dakatar da shiga yajin aikin sai baba...

Wani wanda ya gama jami’a ya yi yunkurin kashe kansa saboda rashin ba shi satifiket É—insa

Wani wanda ya kammala karatun digiri a jami’ar Ambrose Ali da ke Ekpoma a jihar Edo mai suna Precious Ogbeide ya yi yunkurin kashe...