Kotu ta bawa PDP umarnin hana dakatar da Ortom

Gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom ye samu hukunci kotu da ya hana jam’iyyar PDP korarsa daga jam’iyyar.

Mai shari’a, A I Itoyonyin na babbar kotun jihar Benue, shi ne ya bayar da umarnin a ranar Alhamis biyo bayan karar da aka shigar gabansa mai namba MHC/46/2023 a ranar Laraba.

A karar an saka sunan hukumar zabe ta INEC da kuma jam’iyar PDP a matsayin waÉ—anda ake Æ™ara na farko da na biyu.

A hukuncin da ta yanke kotun ta bayar da umarnin wucin gadi da ya hana PDP “Kora, dakatarwa ko kuma aiwatar da duk wani matakin ladabtarwa akan Ortom.” har ya zuwa lokacin da za ta saurari karar.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...