Kotu Ta Ba ‘Yan Sanda Gaskiya Kan Gayyatar Mailafiya

VOA Hausa

Babban kotun dake jihar Filato a Jos, ta yi watsi da karar da tsohon Mataimakin Babban Bankin Najeriya, Dr. Obadiah Mailafiya ya shigar, inda yake kalubalantar cancantar hukumar ‘yan sanda kan gayyatar da ta yi masa don binciken wasu kalaman da ya furta yayin wata hira da wani gidan rediyo a jihar Legas kan rashin tsaro a kudancin Kaduna.

Mai Shari’a Arum Ashoms, ya dauki tsawon lokaci yana karanta bayanai kan hukuncin, ya ce, hukumar ‘yan sanda na da hurumin gayyatar kowa don samun bayanai.

Obadiah Mailafia 2
Obadiah Mailafia 2

Jagoran lauyoyin dake kare Dr. Obadiah Mailafiya, Barista Yakubu Sale Bawa, ya ce za su yi nazarin hukuncin kafin daukar mataki na gaba.

Lauyan bangaren hukumar ‘yan sandan Najeriya, Barista Michael Mayowa Oladipo, ya ce kotu ta yi adalci, soboda hukumar ‘yan sanda na da ikon neman bayyanai a wurin al’umma, kuma hakkin ‘yan kasa ne su bayar da bayyanai ga ‘yan sanda musamman kan abinda ya shafi harkar tsaro.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...