VOA Hausa—
Mai Shari’a Arum Ashoms, ya dauki tsawon lokaci yana karanta bayanai kan hukuncin, ya ce, hukumar ‘yan sanda na da hurumin gayyatar kowa don samun bayanai.
Jagoran lauyoyin dake kare Dr. Obadiah Mailafiya, Barista Yakubu Sale Bawa, ya ce za su yi nazarin hukuncin kafin daukar mataki na gaba.
Lauyan bangaren hukumar ‘yan sandan Najeriya, Barista Michael Mayowa Oladipo, ya ce kotu ta yi adalci, soboda hukumar ‘yan sanda na da ikon neman bayyanai a wurin al’umma, kuma hakkin ‘yan kasa ne su bayar da bayyanai ga ‘yan sanda musamman kan abinda ya shafi harkar tsaro.


