Kotu Ta Ba ‘Yan Sanda Gaskiya Kan Gayyatar Mailafiya

VOA Hausa

Babban kotun dake jihar Filato a Jos, ta yi watsi da karar da tsohon Mataimakin Babban Bankin Najeriya, Dr. Obadiah Mailafiya ya shigar, inda yake kalubalantar cancantar hukumar ‘yan sanda kan gayyatar da ta yi masa don binciken wasu kalaman da ya furta yayin wata hira da wani gidan rediyo a jihar Legas kan rashin tsaro a kudancin Kaduna.

Mai Shari’a Arum Ashoms, ya dauki tsawon lokaci yana karanta bayanai kan hukuncin, ya ce, hukumar ‘yan sanda na da hurumin gayyatar kowa don samun bayanai.

Obadiah Mailafia 2
Obadiah Mailafia 2

Jagoran lauyoyin dake kare Dr. Obadiah Mailafiya, Barista Yakubu Sale Bawa, ya ce za su yi nazarin hukuncin kafin daukar mataki na gaba.

Lauyan bangaren hukumar ‘yan sandan Najeriya, Barista Michael Mayowa Oladipo, ya ce kotu ta yi adalci, soboda hukumar ‘yan sanda na da ikon neman bayyanai a wurin al’umma, kuma hakkin ‘yan kasa ne su bayar da bayyanai ga ‘yan sanda musamman kan abinda ya shafi harkar tsaro.

More News

Ƴan bindiga sun Æ™one ginin hedkwatar Æ™aramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu Æ´anta’adda da ke da alaÆ™a da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa Æ´an’adda a Borno, wani kwamanda ya miÆ™a wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...