Kotu ta ba wa Emefiele damar yin bulaguro daga Abuja zuwa wasu wurare

Mai shari’a Hamza Muazu na babbar kotun birnin tarayya ya baiwa tsohon gwamnan babban bankin kasa Godwin Emefiele izinin ficewa daga babban birnin tarayya Abuja.

Sai dai kotun ta ce dole ne Emefiele ya ci gaba da zama a kasar.

Emefiele, ta bakin lauyansa, Mathew Bukka, SAN, ya bukaci a sauya sharuddan.

Lauyan hukumar EFCC, Rotimi Oyedepo, SAN, bai nuna turjiyarsa game da haka ba.

Ya shaida wa kotu cewa ta tabbatar da Emefiele ya rubuta alkawari cewa zai ci gaba da zama a kasar idan aka amince da bukatarsa.

Haka kuma an gyara tuhumar da ake yiwa tsohon gwamnan CBN zuwa 20 daga 6.

A yanzu dai tuhume-tuhumen da aka yi wa Emefiele sun hada da laifin cin amana, damfarar saye da kuma hada baki wajen aikata manyan laifuka.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...