Kotu ta ba da umurnin damko Hadiza Gabon cikin gaggawa

Wata babbar kotun majistare da ke Kano ta bai wa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Muhammad Wakili (Singham), umarnin ya damko shahararriyar jarumar fim din Hausan nan mai suna Hadiza Gabon, sakamakon kin amsa kiran da kotun ta yi mata.

A kwanakin baya ne dan uwanta na wasan kwaikwayo, Mustapha Naburaska, ya maka ta a kotu sakamakon zargin barazana da cin zarafi da ya ce jarumar ta masa. Kotun ta nemi Hadiza Gabon da ta gurfana a gabanta amma ta yi kirmisisi ta ki zuwa.

Alkalin kotun majistaren, Muntari Dandago ya kuma umarci CP Singham da ya gabatar da bincike tare duba ko zargin da barazanar da Naburaska ya ke wa jarumar ya kai matakin da za a gabatar da shi a gaban kotu.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...