Kotu ta ɗaure waɗanda suka yi fashi a bankin Offa da ke jihar Kwara a 2018

Mai shari’a Haleemah Salman ta babbar kotun jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin a jiya ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wasu mutane biyar da ke fuskantar shari’a a gaban kotu kan laifin fashin bankin Offa.

Kotun ta kuma yanke wa kowane daya daga cikin wadanda aka yanke wa hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari bisa samunsa da laifin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Wadanda aka yankewa hukuncin su ne Ayoade Akinnibosun, Ibikunle Ogunleye, Adeola Abraham, Salahudeen Azeez da Niyi Ogundiran.

A ranar 5 ga Afrilu, 2018, sun kai hari kan wasu bankunan kasuwanci da ofisoshin ‘yan sanda a Offa, karamar hukumar Offa, inda suka kashe mutane 32, ciki har da ‘yan sanda tara a cikin lamarin. 

Gwamnatin jihar ta gurfanar da wadanda ake tuhumar ne a gaban kotu bisa laifin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, fashi da makami da kuma kisan kai.

More News

Wasu matasa uku da ake zargi da garkuwa da mutum sun gurfana a gaban kotu a Kano

Wasu matasa guda uku sun bayyana a gaban wata kotun majistire dake zamanta a unguwar Gyadi-Gyadi dake Kano inda ake tuhumarsu da zargin  yin...

EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba Darius Ishaku

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta kama Darius Ishaku tsohon gwamnan jihar Taraba kan zargin al-mundahanar kuɗaɗen...

Kotu ta tsare matashi kan zargin lalata da yarinya ƴar shekara 13

Kotun majistare ta Badagry da ke Legas a ranar Alhamis, ta bayar da umarnin tsare wani matashi dan shekara 28, Stanley Amos, da ake...

Gwamnatin Najeriya ta kara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC ‘alawee’ zuwa N77,000

Gwamnatin tarayya ta kara yawan alawus din masu yi wa kasa hidima (NYSC) zuwa N77,000 duk wata, daga Yuli 2024.  Wannan ci gaban ya...