Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kano ta kori Gwamna Yusuf, ta bayyana cewa APC ce ta lashe zaben
A wani a wani mataki da ya zo da abin mamaki, kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kano ta tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf daga mukaminsa tare da ayyana dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Nasir Gawuna a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben da aka yi ranar 18 ga watan Maris.
Wannan hukunci dai ya zo ne bayan da kotun ta cire kuri’u 165,663 da ba su dace ba daga jimillar kuri’un da Gwamna Yusuf ya samu sakamakon rashin hatimi ko sa hannun da ke kan takardun kiri’u.
Hukuncin kotun dai yana da matukar tasiri a fagen siyasar jihar Kano, inda ya haifar da cece-kuce da tattaunawa tsakanin manazarta siyasa da masu ruwa da tsaki.
Hakan ya nuna mahimmancin ingancin zabe da bin doka da oda a demokradiyyar Najeriya.