Ko makiyina bana fatan ya fada hannun yan bindiga – Mustapha Imam

Mustapha Imam daya daga cikin fasinjojin jirgin kasan Abuja-Kaduna da yan bindiga suka sace ya ce yana duba lafiyar yan bindigar lokacin da yake hannunsu.

A yaune dai yan bindigar suka samu damar sakin mutane biyar daga cikin mutanen da suke cigaba da garkuwa da su .

A wani fefan bidiyo da mutumin da ya jagoranci tattaunawar sakinsu, Mallam Tukur Mamu mawallafin jaridar Desert Herald ya fitar ya nuna Mustapha na cewa ko makiyinsa baya masa fatan shiga irin halin da suka samu kansu a hannun yan bindigar.

Imam wanda Farfesa ne a fannin likitanci a Jami’ar Usman Danfodiyo dake Sokoto ya ce yana kula da lafiyar yan bindigar da kuma sauran waÉ—anda aka kama.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]