Gwamnatin Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya ta ce ta kama masu kwarmata wa Ć´an bindiga bayanai ‘informants’ fiye da 100 tun bayan katse layukan sadarwa a faÉ—in jihar.
Gwamnan Jihar Dr Bello Muhammad Matawalle ne ya bayyana haka cikin wata hira ta musamman da BBC a gidansa da ke Gusau babban birnin jihar.
“Toshe duk wata hanyar sadarwa tsakanin masu kwarmata bayanai ga Ć´an bindiga ya yi tasiri sosai domin yanzu mun kama infoma fiye da 100,” in ji gwamna Matawalle.
Tsawon kwana 11 kenan da aka toshe layukan salula a fadin Zamfara, daga cikin matakan da hukumomi suka ɗauka na ƙoƙarin magance matsalolin taro a jihar.
Matakin toshe layukan na sadarwa ya shafi yankunan jihar Katsina da ke makwabtaka da jihar Zamfara.
(BBCHAUSA)