Katse layukan salula na tasiri a Zamfara—Bello Matawalle

Gwamnatin Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya ta ce ta kama masu kwarmata wa Ć´an bindiga bayanai ‘informants’ fiye da 100 tun bayan katse layukan sadarwa a faÉ—in jihar.

Gwamnan Jihar Dr Bello Muhammad Matawalle ne ya bayyana haka cikin wata hira ta musamman da BBC a gidansa da ke Gusau babban birnin jihar.

“Toshe duk wata hanyar sadarwa tsakanin masu kwarmata bayanai ga Ć´an bindiga ya yi tasiri sosai domin yanzu mun kama infoma fiye da 100,” in ji gwamna Matawalle.

Tsawon kwana 11 kenan da aka toshe layukan salula a fadin Zamfara, daga cikin matakan da hukumomi suka ɗauka na ƙoƙarin magance matsalolin taro a jihar.

Matakin toshe layukan na sadarwa ya shafi yankunan jihar Katsina da ke makwabtaka da jihar Zamfara.

(BBCHAUSA)

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...