Kasar Taiwan Ta Amince Da Dokar Auren Jinsi

Kasar Taiwan ta bi sahun wasu kasashen duniya da ke halatta auren jinsi, inda ta daura auren wasu karti biyu a wani gagarumin buki a babban birnin Taipei.

A harabar da aka daura auren, babu masaka tsinke kuma a karon farko kenan da ake daura irin wannan auren tun bayan da wakilan majalisar kasar suka zartas da dokar halatta auren jinsin.

Bayanai sun nuna cewa, shekaru kusan 30 kenan da masu hankoron ganin an halatta auren jinsin a Taiwan ke neman a biya musu bukatarsu.

Matakin na zuwa ne duk da cewa ‘yan adawa sun hau kujeran naki.

Wasu tulin masu kaunar a daura masu auren jinsin na ta rige-rigen zuwa ofishin gwamnati da ke kula da lamarin don gabatar da kansu da zummar yi musu rajista.

Ma’aurata mazansu da mata na ta tsotsan bakin juna da rungume juna a bainal jama’a, bayan halartar bukin daura auren na farko da aka yi.

Wata mace mai suna Huang Mei-yu, kusan ta zuba ruwa a kasa ta sha, inda take cewa, yanzu iyayenta sa daina matsa mata da ta auri namiji, tunda dai gwamnati ta san da zamansu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...