Kar a yi saurin yanke wa gwamnatin Tinubu hukunci—in ji Yakubu Gowon

Tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon, ya yi gargadin cewa kada a yi gaggawar yanke hukunci kan ayyukan gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Gowon ya bayyana haka ne ga manema labarai a fadar shugaban kasa jiya bayan ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa.

Tsohon shugaban kasar ya ce ya shawarci Tinubu da kada ya damu da sukar da ake yi wa gwamnatinsa a halin yanzu.

Dattijon ya ce ya yi wuri a yanke hukunci a kan gwamnatin Tinubu.

Ya ce “To, ina gaya masa cewa babu wani shugaban Najeriya da zai iya kawo wannan matakin kuma bai samu dukkan rahotannin abin da ake fada a kansa ba.”

“Ina ganin gwamnati na iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance matsalolin kasar nan daban-daban.”

Wannnan zuwa ne a daidai lokacin da rayuwa ta yi ƙunci wa ƴan Najeriya yayin da farashin kayayyaki ke ci gaba da yin tashin gwauron zabi.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...