Juyin mulki: Amurka za ta kwashe wasu jami’anta daga Nijar

Wani jami’in ma’aikatar harkokin wajen Amurka ya sanar a jiya Alhamis cewa, kasar Amurka ta yi hayar jirgin da zai kwashe wasu kananan ma’aikatanta daga Jamhuriyar Nijar.

Jirgin wanda kuma a bude yake ga ‘yan kasar Amurka da ke son barin kasar ta yammacin Afirka, zai tashi ne da yammacin ranar Juma’a daga Yamai “idan komai ya tafi daidai,” in ji jami’in da ya shaida wa manema labarai, yana mai magana kan yanayin da ba a bayyana sunansa ba.

Ya kara da cewa ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Nijar sun fara tuntubar wasu ‘yan kasar Amurka da suka yi rajista domin sanin ko suna shirin zama ko kuma su fice daga kasar, mako guda bayan hambarar da shugaba Mohamed Bazoum da jami’an tsaronsa da suka kafa gwamnatin mulkin soja.

Amma akwai Amurkawa da yawa da ba sa son barin, in ji shi.

Wasu Amurkawa sun riga sun shiga jiragen da Faransa da Italiya suka yi hayar a cikin ‘yan kwanakin nan.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...