Jirgin farko ta sauka a filin jirgin saman Gusau

A karon farko jirgin sama ya sauka a filin jirgin saman Gusau da maraicen ranar Lahadi a dai-dai lokacin da birnin ke cigaba da shirin tarbar manyan baki a mako mai zuwa.

Sulaiman Idris mai magana da yawun, Dauda Lawal Dare gwamnan jihar Zamfara ya bayyana cewa jirgin saman kirar Bombadier Challenger 605 mallakin gwamnatin Najeriya ya sauka da karfe 04:30 a filin jirgin saman.

” Wannan za ta zama rana mai tarihi a tarihin jihar Zamfara a yayin da gwamna Lawal ya sheda saukar jirgi na farko a filin jirgin saman Gusau,”a cewar sanarwar da Idris ya fitar.

Jirgin mai rijistar namba  5N FGZ ya sauka a filin jirgin ne domin gwaji ko filin jirgin zai iya karbar jirage kamar yadda dokar hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya ta tanada.

More from this stream

Recomended