Jiragen Birtaniya za su koma sauka Sharm el-Sheikh | BBC news

The plane was on its way to St Petersburg when it crashed

Hakkin mallakar hoto
EPA

Image caption

Jirgin na ka hanyarsa ta zuwa St. Petersburg ne a lokacin da bam ya tashi

Birtaniya za ta mayar da zirga-zirgar jiragen sama tsakanin kasarat da yankin shakatawa na Sharm el Sheikh mai farin jini na kasar Masar.

Kusan shekara hudu da ta gabata aka soke dukkan zirga-zirga zuwa can saboda wani harin bam da aka kai kan wani jirgin sama na Rasha.

Kungiyar IS ce ta dauki alhakin kai harin, wanda yayi sandiyyar mutuwar fiye da mutum 200.

Wani gagarumin sakaci a filin jirgin saman Sharm el Sheikh shekara hudu da ta ganata ne ya bayar da kafar da wasu suka dasa wani bam a cikin jirgin saman Rasha da ke kan hanyarsa ta komawa birnin St. Petersburg.

Dukkan wadanda ke cikin jirgin su 224 wanda samfurin Airbus ne sun rasa rayukansu a lokacin da bam din ya tashi yayin da jirgin ke sararin samaniya.

Birtaniya ce kan gaba wajen dakatar da dukkan jiragen kasarta da sauka a filin na Sharm el Sheikh, matakin da ya fusata gwamnatin Masar.

Kasar ta yi fargabar matakin zai shafi tattalin arzikinta da ya ta’allaka kan yawan bude idanu, musamman daga kasashen yammacin Turai.

Amma sauran kasashe ma sun dauki irin wannan matakin.

Masana harkokin tsaro a yankin sun yi itifakin cewa wasu magoya bayan kungiyar IS ne suka dasa bam a jirgin Rashar…

An shafe shekara hudu kafin Birtaniya ta amince ta kyale jiragenta komawa can, kuma kamfanonin masu harkokin yawon bude idanu sun ce suna duba yiwuwar ci gaba da ba mutane karfin gwuiwar ziyartar Sharm el Sheikh.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...