Birtaniya za ta mayar da zirga-zirgar jiragen sama tsakanin kasarat da yankin shakatawa na Sharm el Sheikh mai farin jini na kasar Masar.
Kusan shekara hudu da ta gabata aka soke dukkan zirga-zirga zuwa can saboda wani harin bam da aka kai kan wani jirgin sama na Rasha.
Kungiyar IS ce ta dauki alhakin kai harin, wanda yayi sandiyyar mutuwar fiye da mutum 200.
Wani gagarumin sakaci a filin jirgin saman Sharm el Sheikh shekara hudu da ta ganata ne ya bayar da kafar da wasu suka dasa wani bam a cikin jirgin saman Rasha da ke kan hanyarsa ta komawa birnin St. Petersburg.
Dukkan wadanda ke cikin jirgin su 224 wanda samfurin Airbus ne sun rasa rayukansu a lokacin da bam din ya tashi yayin da jirgin ke sararin samaniya.
Birtaniya ce kan gaba wajen dakatar da dukkan jiragen kasarta da sauka a filin na Sharm el Sheikh, matakin da ya fusata gwamnatin Masar.
Kasar ta yi fargabar matakin zai shafi tattalin arzikinta da ya ta’allaka kan yawan bude idanu, musamman daga kasashen yammacin Turai.
Amma sauran kasashe ma sun dauki irin wannan matakin.
Masana harkokin tsaro a yankin sun yi itifakin cewa wasu magoya bayan kungiyar IS ne suka dasa bam a jirgin Rashar…
An shafe shekara hudu kafin Birtaniya ta amince ta kyale jiragenta komawa can, kuma kamfanonin masu harkokin yawon bude idanu sun ce suna duba yiwuwar ci gaba da ba mutane karfin gwuiwar ziyartar Sharm el Sheikh.