Jiragen ƙasa za su fara aiki da daddare a Najeriya

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Najeriya ta kammala shirin fara gudanar da ayyukan dare kafin karahen watan shida na shekarar 2024.

Manajan Darakta na NRC, Fidet Okhiria, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a ranar Litinin.

Ya fara da cewa, “Abin da ya takaita mana ayyukanmu shi ne aikin dare, kuma ba haka ya kamata jiragen kasa su rika aiki ba. Jirgi ana so yana aiki ne a kowane lokaci. Mutane na iya son yin tafiye-tafiye da yamma, amma saboda yanayin tsaro a kasar, sai mu takaita da rana.

“Muna da niyyar dawo da fasinja da jiragen dakon kaya daga Fatakwal zuwa Aba, Legas zuwa Kano, da kuma Kaduna saboda tashoshi kan tudu,” in ji Okhiria.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...