Jiragen ƙasa za su fara aiki da daddare a Najeriya

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Najeriya ta kammala shirin fara gudanar da ayyukan dare kafin karahen watan shida na shekarar 2024.

Manajan Darakta na NRC, Fidet Okhiria, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a ranar Litinin.

Ya fara da cewa, “Abin da ya takaita mana ayyukanmu shi ne aikin dare, kuma ba haka ya kamata jiragen kasa su rika aiki ba. Jirgi ana so yana aiki ne a kowane lokaci. Mutane na iya son yin tafiye-tafiye da yamma, amma saboda yanayin tsaro a kasar, sai mu takaita da rana.

“Muna da niyyar dawo da fasinja da jiragen dakon kaya daga Fatakwal zuwa Aba, Legas zuwa Kano, da kuma Kaduna saboda tashoshi kan tudu,” in ji Okhiria.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...