
Tawagar gwamnatin tarayya ta isa kasar Saudiya domin karbar gawar marigayi, Aminu Dantata gabanin yi masa jana’iza a birnin Madina.
A ranar Asabar ne Allah ya yi wa marigayi Aminu Dantata rasuwa a birnin Abu Dhabi na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa yana da shekaru 94 a duniya.
Tawagar ta tashi daga Najeriya a ranar Lahadi inda suka isa Madina da tsakar daren ranar Litinin.
Ministan tsaron Najeriya, Muhammad Badaru Abubakar shi ne wanda ya jagoranci yan tawagar da ta kunshi, ministan shari’a Lateef Fagbemi, ministan yada labarai, Muhammad Idris Malagi da kuma karamin ministan gidaje, Yusuf Abdullahi Ata.
Sauran yan tawagar sun hada da Sheikh Dr Bashir Aliyu Umar, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da kuma limamin Masallacin Juma’a na Dantata dake Abuja, Khalifa Abdullahi Muhammad.
A wani lokaci ne nan gaba a ranar Litinin ake sa ran yin jana’izar marigayin bayan da hukumomin Saudiya suka amince a binne gawarsa a can.