Jami’an tsaro sun kashe mayaka IPOB uku a Enugu

Rundunar yan sandan jihar Enugu ta ce yan bindiga uku aka kashe a wani farmaki da aka kai maboyar yan ta’addar kungiyar IPOB.

A wata sanarwa ranar Juma’a, Daniel Ndukwe mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce jami’an rundunar sun yi artabu da yan bindigar a kauyen Imufu dake karamar hukumar Igbo-Eze North ta jihar.

Ndukwe ya ce an gudanar da farmakin tare da hadin gwiwar sojoji na musamman da kuma jami’an DSS a ranar 10 ga watan Agusta.

Ya kara da cewa binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa yan bindigar su ne suka kashe wasu yan bijilante a ranar 21 ga watan Yuli.

Har ila binciken ya nuna cewa yan bindigar su ne ke ta kokarin tabbatar da sai anbi dokar hana fita a yankin karamar hukumar.

An gano tarin makamai da wasu bindigogi a maboyar yan ta’addar.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...