Jami’an gwamnatin Birtaniya fiye da 42 sun yi murabus

Ministocin gwamnati a Birtaniya sun shafe daren jiya suna ganawa da firaminista Boris Johnson a fadarsa na gida mai lamba 10 Titin Downing – domin su lallaba shi ya sauka daga mukaminsa, yayin da sauran goyon bayan da yake da shi a jam’iyyar Conservative mai mulkin kasar ke raguwa.

BBC ta gano cewa daya daga cikin makusantansa – Sakatariyar harkokin cikin gida Priti Patel – na cikin wadanda ke lallaba shi ya yi murabus.

Mista Johnson dai ya kori Michael Gove, daya daga cikin manyan ministocinsa, wanda a baya ke kare gwamnatinsa amma a yanzu ya juya masa baya.

Sam Freedman, wani tsohon mai ba Mista Gove shawara yayin da yake karamin minista na Ilimi ya bayyana mamakinsa ga yadda Mista Johnson ke mayar da martani:Bayan da mutum arba’in da biyu suka ajiye mukami, korar wani mutumin na daban yayi kama da rashin dabara. Sai dai abin mamakin shi ne ya kori Gove ne – mutumin da suka shaku kuma suka dade tare, kuma wannan alama ce ta yadda ikon Mista Boris ke kara rugujewa ta kowane bangare.Duk da ajiye mukamai da jami’an wannan gwmanatin ta Birtaniya suka yi, ciki har da ajiye mukamin da manyan ministoci biyu suka yi, Mista Johnson ya kafe cewa ba zai mika wuya ba.Sakataren kiwon lafiya Sajid Javid da sakataren baitulmali Rishi Sunak ne suka kunna wutar wannnan rikicin na siyasa bayan da suka ce sun gane firaministan ba zai iya sauke nauyin da al’ummar Birtaniya suka dora masa ba.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...