Jami’an gwamnatin Birtaniya fiye da 42 sun yi murabus

Ministocin gwamnati a Birtaniya sun shafe daren jiya suna ganawa da firaminista Boris Johnson a fadarsa na gida mai lamba 10 Titin Downing – domin su lallaba shi ya sauka daga mukaminsa, yayin da sauran goyon bayan da yake da shi a jam’iyyar Conservative mai mulkin kasar ke raguwa.

BBC ta gano cewa daya daga cikin makusantansa – Sakatariyar harkokin cikin gida Priti Patel – na cikin wadanda ke lallaba shi ya yi murabus.

Mista Johnson dai ya kori Michael Gove, daya daga cikin manyan ministocinsa, wanda a baya ke kare gwamnatinsa amma a yanzu ya juya masa baya.

Sam Freedman, wani tsohon mai ba Mista Gove shawara yayin da yake karamin minista na Ilimi ya bayyana mamakinsa ga yadda Mista Johnson ke mayar da martani:Bayan da mutum arba’in da biyu suka ajiye mukami, korar wani mutumin na daban yayi kama da rashin dabara. Sai dai abin mamakin shi ne ya kori Gove ne – mutumin da suka shaku kuma suka dade tare, kuma wannan alama ce ta yadda ikon Mista Boris ke kara rugujewa ta kowane bangare.Duk da ajiye mukamai da jami’an wannan gwmanatin ta Birtaniya suka yi, ciki har da ajiye mukamin da manyan ministoci biyu suka yi, Mista Johnson ya kafe cewa ba zai mika wuya ba.Sakataren kiwon lafiya Sajid Javid da sakataren baitulmali Rishi Sunak ne suka kunna wutar wannnan rikicin na siyasa bayan da suka ce sun gane firaministan ba zai iya sauke nauyin da al’ummar Birtaniya suka dora masa ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...