Jami’an EFCC sun kai samame gidajen kwanan ɗaliban UDUS

Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun kai wani samame da tsakar dare a kan gidajen kwanan dalibai na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato (UDUS), wanda ya kai ga kame wasu dalibai da sanyin safiyar Asabar.

Rahotanni sun bayyana cewa an kai samamen ne a yankin Kwakwalawa da Gidan Yaro, yankunan da daliban jami’a suka fi yawa a Sakkwato. 

Kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, jami’an EFCC sun kai farmaki gidajen kwanan dalibai da misalin karfe 4 na asuba, inda suka damke dalibai da dama.

Wani dalibi ya ce, “Sun zo da asuba, suka shiga dakunanmu, suka fara kama mu ba tare da wani bayani ba.” 

Har yanzu dai hukumar EFCC ba ta fitar da wata sanarwa dangane da samamen ba ko kuma ta bada dalilan da suka sa aka kama su.

Lamarin dai ya yi kama da wani samamen da aka kai a watan Fabrairu a Jami’ar Fasaha ta Tarayya da ke Akure (FUTA) a Jihar Ondo, inda jami’an EFCC suka kama dalibai a wani samame da tsakar dare da ke wajen harabar jami’ar.

More News

Sojoji sun kama ƴan bindiga biyu da suka je asibiti a duba lafiyar su

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun samu nasarar kama wasu ƴan bindiga biyu dai-dai lokacin da suka je asibiti domin a duba lafiyar su a...

Sojoji sun kama ƴan bindiga biyu da suka je asibiti a duba lafiyar su

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun samu nasarar kama wasu ƴan bindiga biyu dai-dai lokacin da suka je asibiti domin a duba lafiyar su a...

Gwamnatin tarayya ta sanar da ranar hutun bikin samun ƴancin kai

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Talata, 1 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutun bikin tunawa da ranar da Najeriya ta samu ƴan cin...

Wasu matasa uku da ake zargi da garkuwa da mutum sun gurfana a gaban kotu a Kano

Wasu matasa guda uku sun bayyana a gaban wata kotun majistire dake zamanta a unguwar Gyadi-Gyadi dake Kano inda ake tuhumarsu da zargin  yin...