Jakadan Najeriya a kasar Maroko, Mansur Nuhu Bamalli ya rasu yana da shekaru 42.
Bamalli wanda tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari ya naÉ—a muÆ™amin jakada a shekarar 2022 ya kasance mataimakin darakta a ma’aikatar harkokin kasashen waje kafin naÉ—in nasa.
Marigayin kanine ga sarkin Zazzau na yanzu, Ahmad Nuhu Bamalli kana shi ne ke rike da sarautar Magajin Garin Zazzau har ya zuwa lokacin mutuwarsa.
Wata sanarwa da masarautar Zazzau ta fitar ta bayyana cewa marigayin ya rasu ne a wani asibiti dake Lagos lokacin da yake kan hanyarsa ta komawa ƙasar Maroko.