Jagororin ADC Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Don Ceto Dimokuradiyyar Najeriya A Abuja

Fitattun ‘yan jam’iyyar haɗaka ta ADC, ciki har da Atiku Abubakar, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso, sun jagoranci zanga-zangar nuna adawa da matakin hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, a yau, Laraba.

Sauran manyan jiga-jigan jam’iyyar da suka shiga zanga-zangar sun haɗa da tsohon gwamnan jihar Rivers, Rotimi Amaechi, tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mar, tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Tambuwal.

Magoya bayan jam’iyyar daga jihohi daban-daban, ciki har da mambobin Kwankwasiyya, sun halarci taron domin miƙa wata wasika mai ɗauke da korafe-korafe, ciki har da kiran shugaban INEC ya yi murabus.

Zanga-zangar ta fara ne daga Maitama Roundabout a Abuja, inda ta ƙare a hedikwatar INEC. Masu zanga-zangar na zargin hukumar zaben da yin aiki tare da jam’iyyar APC mai mulki domin kawo cikas ga dimokuradiyyar ƙasar.

An ga Amaechi yana cikin mota yana yi wa masu zanga-zangar jawabi yayin da suke tafiya a titunan babban birnin ƙasar. A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya nuna hotuna da bidiyo yayin da yake tare da sauran masu zanga-zangar.

More from this stream

Recomended