Isra’ila da Bahrain sun kulla huldar diflomasiyya a hukumance

An shafe shekaru ba a ga maciji tsakanin kasashen larabawa da Isra'ila a gabas ta tsakiya.

Kasashen Isra’ila da Bahrain sun kulla yarjejeniyar diflomasiyya a hukumance, a wani biki da a ka gudanar a babban birnin Bahrain wato Manama a jiya Lahadi.

Yarjejeniyar wadda Amura ta samar ta kawo karshen zaman doya da manja da a ka shafe shekaru a na yi a tsakanin kasashen biyu.

An shafe shekaru ba a ga maciji tsakanin kasashen larabawa da Isra’ila a gabas ta tsakiya.

A baya kasashen sun kafe cewa ba za su shirya da Isra’ila ba har sai ta daidaita da Falasdin.

A yanzu Bahrain ta zamo kasa ta hudu a Gabas ta Tsakiya da ta maido da huldar diflomasiyya bayan kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da Masar da Jordan.

Ba a jima ba da a ka gudanar da irin wannan biki tsakanin Isra’ila da Hadaddiyar Daular Larabawa.

Kuma shi ne karon farko da kasashen su ka aminta da kafuwar Isra’ila tun bayan samar da ita a shekarar 1948.

To sai dai Falasdinawa sun yi tir da kasar Bahrain kan abin da ta kira ‘zamba cikin aminci’.

Jim kadan bayan kulla yarjejeniyar, ministan harkokin wajen Bahrain Abdullatif bin Al-Zayani ya ce fatan su shine ‘a samu hadin kai mai dorewa ta fuskar diflomasiyya a tsakanin kasashen biyu’.

Tun a watan da ya gabata ne Falasdin ta janye jekadan ta da ke Bahrain, bayan da ta fito fili cewa gwamnati a Manama na shirin maido da hulda da Isra’ila.

Hakama kawance ba zai yi wa Iran dadi ba, da tsoron cewa kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain da Saudiyya da kuma Isra’ila a yanzu za su hade mata kai.

(BBC Hausa)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...