
Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya, NAHCON ta ce dukkanin alhazan Najeriya za su dawo gida nan da ranar 28 ga watan Yuni duk da tsaikon da ake samu a yanzu a aikin jigilar dawo da alhazan.
A wata sanarwa ranar Laraba, Fatima Usara mataimakiyar daraktan yada labarai a hukumar ta ce rashin saurin da ake samu wajen kwaso alhazan ya samo asali ne saboda karancin gurbin sauka da tashin jirage a filin jirgin saman Jeddah saboda yadda kowace kasa ke kokarin kwashe nata alhazan.
Ta ce Najeriya ba a bata gurbin jirage da yawa ba duk da yawan alhazan da take da su amma ana cigaba da tattaunawa da hukumomin kasar Saudiya domin samun jadawali mai kyau.
Sanarwar ta ce kamfanin jiragen sama na Flynas shi ne kadai yake da gurbin tashin jirage biyu a kowace rana amma kuma hukumar na cigaba da kokarin ganin kamfanonin jiragen sama na Air Peace, Umza da kuma Max Air sun samu gurabe masu kyau.
Ta kara da cewa tun da akwai jirage masu girma aikin jigilar dawo da alhazan zai gudana a cikin sauri da zarar komai ya dai-daita.