Hukumar Hisbah ta kama mabarata 643 a Kano – AREWA News

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu mutane 643 da aka samu da yin barace-barace a wasu tituna na birnin jihar.

Ana zargin su ne da karya dokar jihar da aka kafa a watan Fabrairu da ta hana yin bara a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar,Lawan Ibrahim ya ce an kama mutanen ne a yankin Bata,titin Murtala Muhammad, Asibitin Nasarawa, Tashar jirgin kasa da kuma gaban Yahuza suya.

Yace wadanda aka kama sun haɗa da mata 416 da kuma maza 232.

Ibrahim ya ce hukumar zata cigaba da kama marabata da suke cigaba da karya dokar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...