Hukumar Asibiti A Sokoto Sun Karyata Labarin Bullar Bakuwar Cuta

Hukumomin Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo dake Sokoto sun ce babu wata bakuwar cuta da ta bulla a asibitin.

Shugaban asibitin koyarwar, Dr.Anas Sabir shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na asibitin, Mallam Buhari Abubakar ya fitar a Sokoto ranar Asabar.

Sabir ya ce karin hasken ya zama dole idan aka yi duba da wani fefan muryar wani da ba a san kowaye ba da ake yadawa a gari dake cewa wani mara lafiya da aka kawo daga jihar Kaduna ya mutu sanadiyar wata bakuwar cuta kwanaki kadan bayan an kwantar da shi a asibitin.

Ya ce mutumin da ya yi kalaman ya alakanta majiyarsa da wasu gidajen rediyo biyu dake jihar inda ya yi kirarin cewa karin wasu marasa lafiya 15 sun mutu a asibitin sanadiyar cutar.

“Domin kawar da duk wani shakku hukumomin asibiti suna so su bayyana a fili karara cewa har kawo wannan lokaci yanzu basu karbi mai wannan cuta daga Kaduna ko wani wuri a kasarnan.” a cewar sanarwar.

Sanarwar ta cigaba da cewa ikirarin da aka ji a cikin fefan muryar da ake yadawa bashi da tushe bare makama karya ce tsagwaronta.

More News

Wani jami’in kwastam ya harbe kansa har lahira a Kano

Wani jami'in hukumar kwastam ya harbe kansa har lahira a gidansa dake unguwar Farm Centre a cikin birnin Kano. Mai magana da yawun rundunar Æ´an...

Wani jami’in kwastam ya harbe kansa har lahira a Kano

Wani jami'in hukumar kwastam ya harbe kansa har lahira a gidansa dake unguwar Farm Centre a cikin birnin Kano. Mai magana da yawun rundunar Æ´an...

Peter Obi Ya Ziyarci Atiku Da Sule Lamido A Abuja

Peter Obi ɗantakarar shugaban ƙasa a jam'iyar LP a zaɓen shekarar 2023 ya ziyarci tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar a. Abuja ranar Litinin. Atiku...

Wani mutumi ya yi garkuwa tare da kashe Æ´ar’uwarsa a Kaduna

A ranar Lahadin ne mazauna birnin Zariya na jihar Kaduna suka shiga alhini cikin alhini sakamakon kama wani mai suna AbdulAzeez Idris da ake...