Hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, ta yi barazanar kame kayan da aka boye tare da gurfanar da masu aikata wannan laifin a gaban kuliya.
Shugaban hukumar Muhyi Rimingade ne ya yi wannan barazanar a ranar Alhamis yayin da yake yi wa manema labarai karin haske kan hauhawar farashin kayayyaki a fadin kasar.
A cewarsa, hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kwace kayayyakin da aka boye tare da gurfanar da masu laifin a gaban kuliya.
Ya yi bayanin cewa hukumar za ta dauki kwakkwaran mataki kan daidaikun mutane ko ’yan kasuwa da aka samu suna tara kayan masarufi domin a samun riba mai yawa a kai.