Har yanzu ba a fara ɗebe ƴan Najeriya da ke Sudan ba

Rahotannin da muke samu sun nuna cewa har yanzu ba a fara ɗebe ƴan Najeriya da ke Sudan ba duk da alkawarin da gwamnati ta yi.

In ba a manta ba ana cikin mawuyacin hali a kasar ta Sudan saboda yakin da ake fama da shi wanda ya dauki tsawon makonni.

Jaridar Daily Trust ta ambato shugaban ɗaliban Najeriya da ke Sudan yana cewa har zuwa daren jiya gwamnatin ba ta fara shirye-shiryen ɗebe daliban ba.

Zuwa yanzu dai an hallaka daruruwan mutane a dalilin yaƙin da ya barke tsakanin dakaru masu kare gwamnati da ƴan adawa.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...