Gwamnonin APC na zawarcin Wike

A yanzu dai za a iya cewa gwamnan jihar Rivers,Nyesom Wike ya zama turare dan goma ganin yadda kowane bangare na manyan Jam’iyun APC da PDP ke neman ya kasance tare da su.

A yayin da jam’iyar PDP ke kokarin yin duk me yiyuwa domin ganin Wike bai sauya sheka ba ita kuwa jam’iyar APC zawarcin gwamnan take domin ya dawo cikinta.

Koda a ranar Juma’a sai da wasu gwamnonin jam’iyyar uku suka kai masa ziyara.

Gwamnonin sun hada da,Kayode Fayemi na Ekiti,Babajide Sanyaolu na jihar Lagos da kuma Rotimi Akeredolu na jihar Lagos.

More from this stream

Recomended