Gwamnatin Zamfara ta ba wa ma’aikatanta romon karshen shekara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da biyan albashin watan 13 ga dukkan ma’aikatan gwamnati a jihar.

Gwamnati ta sanar da hakan ne a ranar Alhamis a wata sanarwa da shugaban ma’aikata, Ahmed Liman ya fitar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Idris, ta bayyana hakan a matsayin babban lamari wanda ya yi daidai da kudurin gwamnati na jin dadin ma’aikata da kuma kara zaburar da ma’aikata.

Sanarwar ta kara da cewa, “A yau, Gwamna Dauda Lawal ya amince da biyan kudaden lamuni na karshen shekara ga jama’a da ma’aikatan gwamnati a jihar Zamfara.

“Ya kamata a lura cewa wannan shi ne karo na farko a tarihin Zamfara da gwamnatin jihar ke biyan ma’aikata albashin watan 13.”

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...