Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925 ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya a karkashin shirin samar da gidaje na ƙasa.
Marcus Ogunbiyi babban sakataren ma’aikatar gidaje da bunÆ™asa birane shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja.
Ranar 1 ga watan Nuwamban 2023 gwamnatin tarayya ta ware naira biliyan 50 domin gina gidaje 40,000.
Ogunbiyi ya ce an kammala rabon gidajen na rukunin farko bayan sake duba sharuda da kuma hanyar da za abi wajen sayar da gidajen.