Sakamakon barkewar cutar anthrax a wasu kasashe da ke makwabtaka da ƙasar nan, an shawarci ‘yan Najeriya da su daina cin naman daji da ganda.
Ma’aikatar Gona da Raya Karkara ta Tarayya ce ta bayar da wannan gargadi a ranar Litinin a wata sanarwa mai dauke da sa hannun Dr. Ernest Umakhihe, babban sakataren ma’aikatar.
Umakhihe ya yi nuni da cewa, akwai bukatar a sanar da ‘yan Najeriya game da bullar cutar da ke ci gaba da yin barna a arewacin Ghana, mai iyaka da Burkina Faso da Togo.
Ya bayyana cewa anthrax yana yaduwa daga dabbobi marasa lafiya zuwa mutane tun da cutar ta kasance a cikin ƙasa kuma akai-akai tana cutar da na gida da na daji.
Alamominta sun haɗa da alamun mura kamar tari, zazzaɓi, da ciwon tsoka, kuma idan ba a gano shi ba kuma a yi saurin magance shi, yana iya haifar da ciwon huhu, matsalolin huhu mai tsanani, wahalar numfashi, firgita, har ma da mutuwa.