Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranar Hutun Dimakwaradiya

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Alhamis a matsayin ranar hutun dimakwaradiya na shekarar 2025.

Olabunmi Tunji-Ojo ministan harkokin cikin gida shi ne ya sanar da haka a ranar Lahadi a cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar din-din ta ma’aikatar, Magdalene Ajani ta sanyawa hannu.

Ministan ya taya yan Najeriya murna shafe shekaru 26 a jere  karkashin mulkin dimakwaradiya kana ya jinjina musu kan yadda su ke cigaba da nuna juriya da jarumtaka.

Tunji-Ojo ya ce Najeriya karkashin jagorancin shugaban kasa Tinubu na cigaba da bin ginshikan dimakwaradiya ta yadda ra’ayin da yan kasa ke bayyana ke tafiyar da alkiblar kasar ta bangaren tattalin siyasa da kuma zamantakewa.

More from this stream

Recomended