Gwamnatin tarayya ta hana sayar da iskar gas ƙasashen waje

Gwamnatin tarayya ta sanar da hana sayar man iskar gas na LPG da ake girki da shi ya zuwa ƙasashen waje.

Ekperikpe Ekpo ƙaramin ministan harkokin mai ɓangaren iskar gas shi ne ya sanar da haka ranar Alhamis a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki.

Ya ce matakin an ɗauke shi ne da gangan domin tabbatar da wadatuwar iskar a kasuwar cikin gida da kuma sauƙaƙawa mutane saboda yadda gas ɗin yayi tsada.

Ya ƙara da cewa tabbas idan aka samu wadatuwar iskar gas ɗin to kuwa babu makawa farashinsa zai yi ƙasa.

” Ina magana da hukumar NMDPRA dake saka ido muna yin taruka kusan kullum da kuma kamfanonin da suke samar da gas irinsu Shell,Mobil da Cheveron akwai fatan cewa abubuwa za su canza. Bama buƙatar muyi ta surutu akan batun.” Ya ce

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...