Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutun Kirsimeti Da Na Sabuwar Shekara

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 25 da kuma ranar Talata 26 ga watan Disamba 2023 sai kuma ranar Litinin 1 ga watan Janairun 2024 a matsayin ranakun bikin hutun kirsimeti da na sabuwar shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olabunmi Tunji Ojo shi ne ya bayyana haka a maddin gwamnatin tarayya a cikin wata sanarwa ranar Juma’a mai dauke da sa hannun, Peter Egbodo mai rikon mukamin babban sakatare a ma’aikatar.

Ministan ya taya al’ummar kirista murnar bikin na kirsimeti kana ya shawarce su da su yi koyi da Yesu Kiristi kan halayen da ya aikata da kuma wadanda ya koyar.

Ya kara jaddada cewa tsaro da zaman lafiya su ne ginshikin cigaban tattalin arziki da kuma cigaba.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu É“atagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an Æ´an sanda da haÉ—in gwiwar Æ´an bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...