Gwamnatin Najeriya za ta biya alawus ɗin N-Power na wata tara

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na fara biyan bashin watanni tara ga masu cin gajiyar shirin N-Power da ke shirin farawa daga watan Nuwamba.

Ta bayyana hakan ne a ranar Litinin ta bakin Manajan shirye-shiryen N-Power na kasa, Akindele Egbuwalo, wanda ya bayyana hakan a wata ganawa da wasu masu cin gajiyar N-Power a ofishinsa da ke Abuja.

Egbuwalo a wata sanarwa da ma’aikatar kula da jin kai da yaki da fatara ta tarayya ta fitar, ya bayyana cewa babbar manufar dakatar da shirin na wucin gadi shi ne a magance duk wani abu da ya shafi masu cin gajiyar shirin kai tsaye.

A cikin sanarwar ya bayyana cewa, sakamakon dakatar da shirin na wucin gadi da aka yi na yin gyaran fuska da kuma binciken kwakwaf, an kwato kudade daga hannun wasu a ciki.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...