Gwamnatin Kwara Ta Mayar Da Ranakun Aiki Kwana 3 A Mako

Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq a ranar Litinin ya bada umarnin cewa ma’aikatan jihar su rika zuwa aiki sau uku a mako maimakon kwanaki biyar.

Shugabar ma’aikatan jihar,Susan Modupe Oluwole ita ce ta sanar da haka a Ilorin inda ta ce gwamnatin jihar ta amince da rage kwanakin a matsayin matakin wucin gadi na rage raɗadin cire tallafin man fetur da aka yi.

Oluwole ta gargadi ma’aikatan da kada su yi amfani da damar wajen yin sakaci da aiki.

More from this stream

Recomended