Gwamnatin Kano Za Ta Rabawa Ɗaliban Jihar Su 6500 Fom Na Jarrabawar UTME

Gwamnan jihar Kano,Engr Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da shirin raba fom ɗin jarrabawar UTME ga ɗaliban sakandaren jihar dubu 6500.

A wata sanarwa gwamnan ya ce ya yi hakan ne domin samar da damarmaki ga ɗaliban jihar na halartar makarantun da suke gaba da sakandare.

“A ƙoƙarin mu na samar da damarmaki na cigaba da karatun gaba da sakandare ga ƴan asalin jihar Kano na ƙaddamar da rabon fom ɗin jarrabawar JAMB UTME  guda 6500 ga ɗaliban makarantun sakandare,” ya ce.

Ya ce gwamnatinsa ta samu cimma manyan nasarori a bangaren bunƙasa ilimi a jihar a cikin watanni goman da suka gabata da suka haɗa da dawo da shirin tura ƴan asalin jihar ƙaro karatu a jami’o’in ƙasashen waje, biyan kuɗin makaranta na ɗaliban jihar dake manyan makarantu da sake buɗe makarantu 21 na koyon sana’a.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...