Gwamnatin Kano Za Ta Rabawa Ɗaliban Jihar Su 6500 Fom Na Jarrabawar UTME

Gwamnan jihar Kano,Engr Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da shirin raba fom ɗin jarrabawar UTME ga ɗaliban sakandaren jihar dubu 6500.

A wata sanarwa gwamnan ya ce ya yi hakan ne domin samar da damarmaki ga ɗaliban jihar na halartar makarantun da suke gaba da sakandare.

“A ƙoƙarin mu na samar da damarmaki na cigaba da karatun gaba da sakandare ga ƴan asalin jihar Kano na ƙaddamar da rabon fom ɗin jarrabawar JAMB UTME  guda 6500 ga ɗaliban makarantun sakandare,” ya ce.

Ya ce gwamnatinsa ta samu cimma manyan nasarori a bangaren bunƙasa ilimi a jihar a cikin watanni goman da suka gabata da suka haɗa da dawo da shirin tura ƴan asalin jihar ƙaro karatu a jami’o’in ƙasashen waje, biyan kuɗin makaranta na ɗaliban jihar dake manyan makarantu da sake buɗe makarantu 21 na koyon sana’a.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...