Gwamnatin Kano ta yi wa ma’aikata ƙarin girma

Hukumar da’ar ma’aikata ta jihar Kano ta amince da karin girma ga manya da kananan ma’aikata 118 a ma’aikatu da sassa da hukumomi 13.

Shugaban hukumar Dr Umar Shehu Minjibir ne ya bayyana hakan bayan zaman hukumar a Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na hukumar Musa Garba ya fitar jiya.

Dokta Minjibir ya ci gaba da cewa adadin wadanda aka yi wa karin girma tun bayan kaddamar da hukumar da ya jagoranta a watan Agustan wannan shekara sun kai 379.

A yayin da yake yabawa da jajircewar ma’aikatan a fadin hukumar, shugaban ya yi kira ga ma’aikatan da aka kara musu girma da su maida hankali wajen yin aiki tukuru domin samun sakamako mai kyau.

More News

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...