Gwamnatin jihar Kaduna ta kafa kwamitin biyan diyya ga mutanen da harin jirgin sama ya shafa

Gwamnatin jihar Kaduna, ta kafa wani kwamiti da zai biya diyya tare da tallafi ga mutanen da harin jirgin sama marar matuki na rundunar sojan Najeriya ya kai kan mutanen ƙauyen Tudun Biri dake ƙaramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

A ranar Lahadi ne mutane sama da 100 da suka taru a wurin wani taron Maulidi suka gamu da ajalinsu bayan da wani jirgin sama ya sakar musu bam.

Tuni rundunar sojan ta amsa laifin kai harin da tace an kai shi ne a bisa kuskure lokacin da jirgin ke aiki kai hari kan Æ´an ta’ada da su ke a yankin.

A wata sanarwa ranar Talata mataimakiyar gwamnan jihar, Hadiza Balarabe Sabuwa ta sanar da kafa kwamitin lokacin da ta jagoranci tawagar wakilan gwamnati ya zuwa ƙauyen.

Hadiza ta ce kwamitin zai Æ™unshi manyan jami’an gwamnati, shugabanni addini da kuma wakilan rundunar sojan Najeriya.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuÉ—aÉ—e

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...