Gwamnatin Borno za ta garambawul wa tsarin zaɓen ƙananan hukumomi

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya bayyana shirinsa na sake fasalin tsarin zaben kananan hukumomin jihar domin samar da dama ga mutanen ‘masu gaskiya’ su tsaya takara.

Gwamnan ya bayyana haka ne a garin Mafa da ke karamar hukumar Mafa a jihar Borno a ranar Asabar, inda ya kara da cewa gyaran tsarin zai tabbatar da cewa masu kada kuri’a za su zabi mafi kyawun abin da suke so.

Zulum ya kada kuri’a a mazabar Ajari II mai lamba 006 a Mafa Ward, hedkwatar karamar hukumar.

Ya ci gaba da cewa, “Dole ne a inganta tsarin zabenmu, sannan a yi adalci sannan kuma muna bukatar masu gaskiya su tsaya takara, sannan muna son masu kada kuri’a da za su iya bambantawa, masu kada kuri’a za su iya zabar mafi inganci ba tare da son rai ba.”

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...