Gwamnan Kogi ya ba da umurnin rufe asusun jiha da na kananan hukumomi

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayar da umarnin rufe asusun ajiyar kananan hukumomi da na jihar nan take.

Wata sanarwa da kwamishinan kudi, Asiwaju Asiru Idris ya fitar ta tabbatar da hakan.

Sanarwar ta ce: “Ba za a yi wa kowa wani abu ko wani nau’i na biyan kudi daga Asusun Gwamnati ba.

“An soke umarnin tsayawa da kuma umarnin saka hannun jari nan da nan.”

Ya zuwa yanzu Arewa.ng ba ta samu wata sanarwa da ta bayyana dalilin daukar wannan mataki ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]